Isa ga babban shafi

'Yan majalisar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun soke hukuncin kisa

'Yan majalisar dokokin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun kada kuri'ar amincewa da soke hukuncin kisa, matakin da suka aiwatar a ranar Juma'ar da ta gabata.

Fasalin igiyar da ake rataye masu laifin da hukuncin kisa ya hau kansu.
Fasalin igiyar da ake rataye masu laifin da hukuncin kisa ya hau kansu. © REUTERS
Talla

A halin da ake ciki, kallo ya koma ga shugaba Faustin-Archange Touadera, wanda dole sai ya sanya hannu kan sabuwar dokar ta soke hukuncin kisa a kasar kafin ta tabbata.

Kasar dai ta bi sahun Chadi a shekarar 2020 da Saliyo a shekarar bara wajen kawo karshen hukuncin kisa a nahiyar Afirka a shekarun baya bayan nan.

Hukuncin kisa na karshe da aka zartas a Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ya kasance a shekarar 1981.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.