Ghana ta fara wayar da kan jama'arta game da barazanar shigar 'yan ta'adda
Hukumomin tsaron Ghana sun yi gargadi ga jama’ar kasar a game da yiwuwar shigar ‘yan ta’adda kasar, la’akari da yadda ayyukan su ke kamari a kasashe makotan Ghana. Wannan ta sa tuni Limaman Masallatai da na majami’u suka dauki gabarar wayar da kan jama’a da kuma tsaurara matakan tsaro. Wakilinmu na Ghana Abdallah Sham-un Bako na dauke da karin bayani.
Wallafawa ranar:
Kunna - 02:55