Shugaban Tunisia ya rusa majalisar dokokin kasar
Shugaban Tunisia Kais Sa’id ya rusa majalisar dokokin kasar wadda ya dakatar da ayyukanta kimanin watanni 8 da suka gabata, matakin da ke ya kara jefa kasar a cikin wadi na rikicin siyasa.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaba Kais ya sanar da rusa majalisar ne a jawabin da ya gabatar cikin daren jiya, sa’o’i kadan bayan da aka ruwaito cewa ‘yan majalisar sun gudanar da zama ta hoton bidiyo.
Yayin ganawar da suka yi, ‘yan majalisar sanar da cewa sun dawo bakin aiki tare da soke illahirin dokoki na musamman da shugaban ya kafa a watanni 8 da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu