Adadin mutanen da guguwar Batsirai ta kashe sun kai 120
Adadin mutanen da suka mutu sakamakon mahaukaciyar guguwar da ta afkawa kasar Madagascar da aka yiwa suna Batsirai ya kai 120, kuma akasarin wadanda suka mutu sun fito ne daga yanki guda.
Wallafawa ranar:
Hukumar agajin gaggawa ta kasar tace sama da kashi 70 na mamatan sun fito ne daga yankin Ikongo dake kusa da gabashin tsibirin dake kogin India.
Gwamnatin kasar tace guguwar ta shafi mutane 125,000 wajen raba su da matsugunan su, yayin da jami’an jinkai ke can suna taimaka musu wajen samar musu da matsuguni da kuma abinda zasu ci.
Kasar Madagascar na daya daga cikin masu fama da matsalar talauci a duniya, yayin da sama da kashi 42 na yara kasar ke fama da matsalar yunwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu