Isa ga babban shafi
Madagascar

Adadin mutanen da guguwar Batsirai ta kashe a Madagascar ya kai 92

Adadin mutanen da mahaukaciyar guguwar da aka yiwa suna Batsirai ta kasha a kasar Madagascar ya kai 92, yayin da kungiyoyin agaji ke ci gaba da kokarin taimakawa mutane sama da 110,000 dake bukatar agajin gaggawa.

Yadda guguwar Batsirai ke ci gaba da barna a Madagascar.
Yadda guguwar Batsirai ke ci gaba da barna a Madagascar. © Alkis Konstantinidis, Reuters
Talla

Ofishin agajin gaggawa a kasar yace adadin mutanen da suka mutu a Yankin Ikongo inda matsalar tafi girma ya kai 71, yayin da mutane sama da 61,000 suka rasa matsugunin su.

Wani dan majalisar da ya fito daga yankin Brunelle Razafintsiandrofa yace akasarin mutanen sun mutu ne sakamakon rushewar da gidajen su suka yi akan su.

Majalisar Dinkin Duniya tare da kungiyoyin agajin sun fara kai kayan agaji ga mutanen da hadarin ya ritsa da su.

Kasar Faransa ta tura jami’an agajin ta 60 domin taimakawa wajen samar da tsaftacaccen ruwan sha a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.