Isa ga babban shafi
Sudan

Kwamitin tsaron MDD zai tattauna kan rikicin kasar Sudan

Wasu majiyoyin jami’an diflomasiyya sun ce a ranar larabar da ke tafe, kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai tattauna kan halin da ake ciki a Sudan, inda dubban ‘yan kasar ke cigaba da zanga-zangar adawa da juyin mulkin da sojoji suka yi.

Yadda sabuwar zanga-zanga ta barke a Sudan bayan murabus din Firaminista Abdalla Hamdok a ranar 2 ga watan Janairun, 2022.
Yadda sabuwar zanga-zanga ta barke a Sudan bayan murabus din Firaminista Abdalla Hamdok a ranar 2 ga watan Janairun, 2022. - AFP
Talla

Majiyoyin sun bayyana cewar kasashe 6 daga 15 masu kujerar dindindin a kwamitin tsaron ne suka nemi yin taron akan abubuwan da ke wakana a Sudan, kuma ganawar ta su za ta gudana ne a sirrance.

Wani jami'i da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, ba a sa ran kwamitin tsaron ya fitar da matsaya guda kan tashin hankalin kasar ta Sudan, la’akari da cewar kasashen China da Rasha za su hau kujerar naki.

A baya dai Rashan da China sun sha jaddada cewa halin da ake ciki a Sudan na rudani tun bayan da sojoji suka kwace iko a ranar 25 ga watan Oktoba, lamari ne na cikin gida, kuma ba ya barazana ga tsaron kasa da kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.