Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Tsakiyar Afrika

Birnannun nakiyoyi na barazana ga ayyukan jinkai a Afrika ta tsakiya

A Jamhuriyar Tsakiyar Afrika, kungiyoyin agaji na ci gaba da bayyana damuwa ganin ta yada wasu yankunan kasar da ke da arzikin ma’adinai ke tattare da hatsari ga kungiyoyin agajin, kasancewa yan tawaye sun dasa nakiyoyi a yankunan.

Jamhuriyar Afrika ta tsakiya na fama da matsalar tarin nakiyoyin da aka birne a karkashin kasa don yakar matsalar tsaro daga 'yan tawaye.
Jamhuriyar Afrika ta tsakiya na fama da matsalar tarin nakiyoyin da aka birne a karkashin kasa don yakar matsalar tsaro daga 'yan tawaye. AFP
Talla

Yankin Arewa maso yammacin Afrika ta tsakiya ya kasance yankin mai tattare da hatsari  ga kungiyoyi masu aikin jin kai dama direbbobin sufuri dake rayuwa  cikin kutsi  inda ake kyautata zaton  kungiyoyi  dauke da makamai sun dasa nakiyoyi saman wadanan hanyoyi..

A farkon shekarar nan ta 2022 daya daga cikin wakilan yan atchaba mai suna  Lagos Yandja  dake aiki a wannan yankin ya sheidawa kamfanin dilancin labaren faransa cewa  saman hanyar Paoua dake da nisan kilometa 500 da babban birnin kasar Bangui, an samu mutuwar daya daga cikin yan atchaba da ya taka nakiya  ya kuma rasa ran sa nan take, ya karasa da cewa aikin na su na tattare da hatsari, a na sa geffen Augustin Ndusha dake aiki da wata kungiyar agaji,ya na tunai da irin ta’asar da nakiya ta yiwa motar da yake cikin ta.

Hukumomin kasar sun yi shelar cewa yanzu kam sun kwace wasu yankuna daga hannun  kungiyoyi masu dauke da makamai, yayinda a zahiri dakarun gwamnati ke fuskantar turjiyya mai karfi daga wadanan kungiyoyi da za mu iya zana yan tawayen 3R, daya daga cikin manyan kungiyoyin yan tawayen Afrika ta Tsakiya da suka dasa nakiyoyi da dama a wadanan yankuna.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.