Isa ga babban shafi
Sudan

Jami'an tsaro sun kashe masu zanga-zanga 4 a Sudan

Majiyoyin kiwon lafiya a Sudan, sun tabbatar da mutuwar mutane 4 bayan da jami’an tsaro suka yi amfani da karfi don tarwatsa tarzomar da aka gudanar yau alhamis a biranen Ondurman da kuma Khartoum fadar gwamnati.

Masu zanga-zangar kin jinin mulkin Soji a Sudan.
Masu zanga-zangar kin jinin mulkin Soji a Sudan. © Marwan Ali, AP
Talla

Dubun dubatar mutane ne suka fito domin kalubalantar gargadin da mahukunta suka yi kan cewa ka da wanda ya fito da nufin gudanar da tarzomar adawa da gwamnatin hadaka da ta hada sojoji da fararen hula a kasar.

Majiyoyin kiwon lafiya a asibitin Arbain das ke Ondurman, sun tabbatar da cewa an shigar da gawarwakin mutane da dama a asibitin, yayin da a hannu daya jami’an tsaro suka gargadi asibiti da ka da ta kuskura ta bai wa motocin daukar marasa lafiya damar shiga sauke wadanda suka samu raunuka.

Tun da farko dai an baza dimbin jami’an tsaro kan titunan Khartum da kuma Ondurman don tabbatar da cewa ba a gudanar da wannan zanga-zanga ba, amma duk da haka sai da dubban mutane suka fito kan tituna.

Su dai masu wannan tarzoma na jaddada adawarsu ne kan cewa, Sudan ba ta bukatar gwamnatin hadaka da za ta kunshi sojoji da fararen hula, zanga-zangar da aka share tsawon watanni ana yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.