Isa ga babban shafi
Libya - Zabe

Libya ta jinkirta wallafa sunayen 'yan takarar zaben shugabancin Libya

Hukumar zaben kasar Libiya ta jinkirta fitar da jerin sunayen 'yan takarar zaben shugabancin kasar da aka shirya zai gudana cikin kasa da makwanni biyu.

Imed al-Sayeh, shugaban hukumar zaben kasar Libya yayin jawabi ga taron manema labarai a birnin Tripoli, ranar 24 ga watan Oktoba.
Imed al-Sayeh, shugaban hukumar zaben kasar Libya yayin jawabi ga taron manema labarai a birnin Tripoli, ranar 24 ga watan Oktoba. Mahmud TURKIA AFP/File
Talla

Kawo yanzu dai babu karin bayani akan dalilan da suka sanya hukumar zaben Libiyar daukar matakin ba, zalika ba ta bayyana sabuwar ranar da zaben zai gudana ba.

Sai dai wasu masu bibiyar lamurran kasar sun ce hakan ba zai rasa nasaba da cewar a karkashin doka zagayen farko na zaben shugaban kasar ba zai yiwu ba a ranar 24 ga watan Disamba saboda 'yan takara na da damar yin yakin neman zabe na tsawon makwanni biyu bayan fitar da jerin sunayen da aka tantance.

A ranar 2 ga watan Disamba wata kotu a Libya ta mayar da dan marigayi Moamer Kadhafi, Seif al-Islam Kadhafi, cikin ‘yan takara bayan soke sunansa da hukumar zabe ta yi a baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.