Isa ga babban shafi
Sudan

Firaministan Sudan ya kori shugabannin 'yan sandan kasar

Fira Ministan Sudan Abdallah Hamdok, ya kori shugabannin rundunar 'yan sandan kasar, bayan da aka kashe fiye da mutane 40 a yunkurin jami’an tsaron na murkushe zanga-zangar da ta biyo bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan jiya.

Fira Ministan Sudan Abdallah Hamdok.
Fira Ministan Sudan Abdallah Hamdok. REUTERS - HANNIBAL HANSCHKE
Talla

Babban hafsan sojan kasar Janar Abdel Fattah al-Burhan ya kwace mulki tare da tsare Hamdok a ranar 25 ga watan Oktoba, kafin daga bisani ya sake shi, bayan da kasashen duniya suka yi Allah wadai da matakin.

Bayan zanga-zangar gama gari ta adawa da sojojin na Sudan da ta gudana ne, gami da matsin lambar manyan kasashen duniya, Al-Burhan ya maida da Firaminista Hamdok kan mukaminsa, a karkashin yarjejeniyar da aka kulla a ranar 21 ga watan Nuwamba.

Likitoci sun ce akalla mutane 42 aka kashe yayin da jami’an tsaro ke kokarin murkushe zanga-zangar adawa da juyin mulkin da aka shafe makwnni ana yi, a kasar ta Sudan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.