Isa ga babban shafi
TUNISIA

Dubban mutane sun yi gangamin goyawa shugaban Tunisiya Kais Saied baya

Dubban magoya bayan shugaban Tunisiya Kais Saied sun yi gangami a babban birnin kasar da wasu biranen a wannan Lahadi don nuna goyon baya ga dakatar da majalisar kasar da kuma yin alkawarin sauya tsarin siyasa, matakin da masu sukar shugaban ke kira juyin mulki.

Magoyan shugaban kasar Tunisia Kais Saied da suka yi gangami a kasar 03/10/21.
Magoyan shugaban kasar Tunisia Kais Saied da suka yi gangami a kasar 03/10/21. © RFI / Amira Souilem
Talla

Zanga -zangar akalla mutane dubu 8 a tsakiyar Tunis ita ce mafi girma da aka gani, idan aka kwatanta da fitowar masu adawa da matakin tun lokacin da Saied ya kwace ikon zartarwa a watan Yuli.

A ranar 25 ga watan Yuli, bayan watanni na rashin jituwar siyasa, shugaba Saied ya kori Firanminista, kana ya dakatar da majalisar dokoki sannan ya karawa kansa karfin ikon.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.