Isa ga babban shafi
Sudan

Sudan ta dakile yunkurin sojojin Habasha na yi mata kutse

Rundunar sojin Sudan ta sanar da dakile yunkurin kutsen da sojojin Habasha suka yi mata a yankin al-Fashaqa da ke kan iyakar kasashen biyu.

Wasu sojojin kasar Sudan yayin aikin sintiri a garin Mokha mai babbar tashar jirgin ruwa.
Wasu sojojin kasar Sudan yayin aikin sintiri a garin Mokha mai babbar tashar jirgin ruwa. AFP/File
Talla

Sanarwar da rundunar sojin sudan ta fitar dai ba ta yi karin bayan ikan arrangamar da dakarun nata suka yi da na kasar ta Habasha ba, illa kawai cewar da ta yi an dakile yunkurinsu na yin kutse daga yankin Umm Barakit a ranar Lahadi.

Kawo yanzu dai kakakin rundunar sojin Habasha Kanal Getnet Adane, bai amsa tambayar da aka yi masa dangane da lamarin ba.

Tashin hankali a kan iyakar Sudan da Habasha ya karu ne tun bayan barkewar rikici a yankin Tigray na arewacin Habasha a shekarar bara wanda ya tagayyara dubban mutane da a yanzu ke gudun hijira a gabashin Sudan.

Rikicin na baya bayan nan tsakanin dakarun na Sudan da na Habasha ya auku ne a wani yankin al-Fashaqa mai albarkar kasar gona inda suka shafe shekaru suna takaddama akai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.