Isa ga babban shafi

Akalla baki 47 suka mutu a gabar ruwan Mauritania

Majalisar Dinkin Duniya tace akalla bakin haure 47 suka mutu a gabar ruwan Mauritania bayan da kwale kwalen su ya kife a ruwa.

Mashigin ruwan Marseille
Mashigin ruwan Marseille Nicolas TUCAT AFP
Talla

Hukumar kula da kaurar baki tace kwale kwalen wanda ya bar Yankin Laayoune dake Yammacin Sahara ranar 3 ga watan Agusta na kan hanyar zuwa tsibirin Canaries mallakar kasar Spain ne lokacin da ya gamu da hadarin.

'Yan Cin rani
'Yan Cin rani JOAQUIN SARMIENTO AFP

Nicolas Hochart na hukumar kula da kaurar bakin ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar injin din kwale kwalen ya gamu da matsala, yayin da yayi ta yawo akan ruwa na makwanni 2 kafin jami’an tsaron dake kula da gabar ruwan Mauritania su gano shi.

Youssef Bouzidi, wani dan cin rani da ya shiga yajin kin cin abnici a Bruxos.
Youssef Bouzidi, wani dan cin rani da ya shiga yajin kin cin abnici a Bruxos. REUTERS - YVES HERMAN

Hochart yace sun yi nasarar gano mutane 7 da suka tsira da ran su.

Majalisar Dinkin Duniya ta dade tana gargadi dangane da hadarin dake tattare da irin wannan tafiya mai hadari wanda Yan Afirka keyi zuwa Turai domin samu rayuwa mai inganci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.