Isa ga babban shafi

Shugaban Congo ya bukaci yan kasar su bayar da hadin kai wajen karbar allurar covid 19

Shugaban kasar Congo Brazzavile Denis Sassou Nguesso a yau lahadi ya yi kira ga daukacin yan kasar da su bada hadin kai na ganin kowanen su ya karbi allurar rigakafin cutar Covid 19.

Shugaban kasar Congo Brazzaville
Shugaban kasar Congo Brazzaville © REUTERS - Olivia Acland
Talla

Shugaban ya ce bayar da hadin kai zai taimaka wajen rage yawan masu kamuwa da cutar a wannan kasa inda alkaluma ke nuna cewa  kusan kashi biyu daga cikin yawan al’umar ne suka karbi wannan allura yanzu haka,duk da cewa wasu mutanen na ci gaba da nuna adawar su a kai.

Shugaban Congo Denis Sassou Nguesso.
Shugaban Congo Denis Sassou Nguesso. REUTERS/Anis Mili/Files

A watan Afrilun shekarar bana gwamnatin wannan kasa ta kaddamar da shirin yiwa yan kasar wannan allura kamar dai sauren kasashen Duniya.

A hukumance sama da mutane dubu 13.300 ne suka kamu da cutar a Congo Brazzaville yayinda 179 suka bakuci lahira.

Birnin Brazzaville na kasar Congo
Birnin Brazzaville na kasar Congo Getty Images - mtcurado

Ko a baya a matakin  yaki da wannan cuta sai da hukumomin kasar tareda yardar kamfanin Air France mallakin kasar Faransa suka cimma yarjejeniya na dakatar da duk wata zirga-zirga daga kasar  zuwa waje,kazzalika daga waje zuwa cikin kasar ta Congo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.