Isa ga babban shafi
Congo Brazzaville

Daya daga cikin yan takara a zaben Congo Brazzaville ya kamu da cutar Covid 19

A Congo Brazzaville akalla mutane  milyan 2 da dubu dari 5 ne za su fito  don kada kuri’ar su a zaben yau lahadi,daya daga cikin yan takara 6  ya kamu da cutar Coronavirus.Shugaban kasar mai ci Denis Sassou Nguesso mai shekaru 77, da ya share kusan shekaru 36 a kan karagar mulkin kasar na daga cikin masu neman wanna kujera.

Daya daga cikin ruhunan zabe a kasar Congo Brazzaville
Daya daga cikin ruhunan zabe a kasar Congo Brazzaville © AP/John Bompengo
Talla

Yanzu haka wasu daga cikin Shugabanin kungiyoyin Farraren hula  tareda hadin gwiwar wasu jam’iyyun adawa na kira ga yan kasar na ganin sun kauracewa zaben na yau lahadi.

Wani dan kasar Congo na kada kuri'ar sa cikin akwatin zabe a Congo Brazzaville
Wani dan kasar Congo na kada kuri'ar sa cikin akwatin zabe a Congo Brazzaville AFP - EDUARDO SOTERAS

Iyalan daya daga cikin yan takara a zaben,wanda da ya bayyana kamuwa da cutar Coronavirus ,Guy Brice  Parfait Colela sun sanar da cewa suna kan hanyar isa da mutumen su kasashen waje don neman magani ganin tsanatar ciwon da yake fama da shi.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.