Isa ga babban shafi

Shugaban Ghana na fuskantar bore daga kungiyoyi da mutanen kasar

Masu hamayya da salon mulkin shugaba Nana Akufo-Ado na kasar Ghana, sun bukaci jama’a su gudanar da zanga-zangar lumana wannan laraba a birnin Accra don samar da gyara dangane da yadda ake tafiyar mulkin kasar a cewarsu.

Wasu daga cikin magoya bayan yan adawa a kasar Ghana
Wasu daga cikin magoya bayan yan adawa a kasar Ghana REUTERS - FRANCIS KOKOROKO
Talla

Wadanda suka tsara zanga-zangar na zargin gwamnatin Akufo-Ado da gazawa a fagen tattalin arziki, yayin da rashawa ke neman dawowa a kasar, kana suka zargin shugaban da saya wa kansa sabon jirgin sama duk da hali na matsi da al’umma ke ciki.

Birnin Accra na kasar Ghana
Birnin Accra na kasar Ghana Getty Images - ruffraido

A cewar shugabanin kungiyoyin kare hakokkin jama’a,gwamnatin kasar ta gaza wajen shawo kan wasu matsalloli  tareda kaucewa alkawura da suka dau a baya, jama’a na rayuwa cikin kutsi da talauci duk da arzikin da kasar keda shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.