Wata kungiyar agaji za ta dakatar da ayyukanta a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
Kungiyar agaji ta Medicins Sans Frontiers ta sanar da cewa za ta dakatar da ayyukanta a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya bayan da kungiyoyin da ke daukar makamai suka yawaita hare-hare a kan ma’aikatanta.
Wallafawa ranar:
Kungiyar ta zargi mayakan da kai hare-hare a kan ma’aikata da ofisoshinta.
A watan Yuni, mayakan sun yi wa ayarin motocin kungiyar Medicins Sans Frontiers kwanton bauna a kan hanyarsa zuwa asibiti, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wata mai kula da mara lafiyar.
Gabanin harin watan Yunin, sai da wasu 'yan bindiga suka kashe ma'aikatan kungiyar Medicins Sans Frontiers 6.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu