Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

An soma taron sasanta rikicin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

An soma taron tattaunawa don kawo karshen mummunan rikicin da ya dabaibaye Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya a Khartoum, babban birnin Sudan.

Wasu mayakan 'yan tawayen Seleka fna Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.
Wasu mayakan 'yan tawayen Seleka fna Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya. REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

Taron da aka fara a ranar Alhamis, na samun halartar wakilan gwamnati da kuma kungiyoyi 14 da suka dauki makamai.

Taron da ke karkashin jagorancin Tarayyar Afirka, shi ne karo na takwas cikin shekaru shida da kungiyar ta yi tanalalubo mafitar kawo karshen rikicin.

Dubban mutane ne suka mutu tun shekarar 2013, kana mutane miliyan 4 da rabi suka tsere daga gidajensu sakamakon rikicin da ya barke a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiyar.

Gwamnatin Sudan ta ce za a shafe makwanni uku ana gudanar da taron, don samun masalaha mai dorewa.

Rikicin Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya yasamo asali ne a shekarar 2013, lokacin da kungiyar ‘yan tawayen Seleka ta kifar da gwamnatin shugaba Francois Bozize, juyin mulkin da yayi sanadin bullar ‘yan tawayen anti-Balaka, wadanda akasarinsu kiristoci ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.