Isa ga babban shafi
Bakin Haure

Bakin haure sama 100 sun kife a gabar ruwar Libya

Fiye da 'yan cirani 100 dake cikin wani kwale-kwale ake fargaban sun mutu a gabar ruwan Libya a kokarinsu na ketarawa zuwa Turai.

Kungiyoyin agaji da suka ceto bakin haure a gabar ruwar Libya  21 da watan Yuni 2016
Kungiyoyin agaji da suka ceto bakin haure a gabar ruwar Libya 21 da watan Yuni 2016 AP - Santi Palacios
Talla

Kungiyoyin agaji masu zaman kansu da hukumar kula da kaura ta Majalisar Dinkin Duniya suka bayyana haka cikin wata sanarwa da suka fitar, adai-dai lokacin da  masu kokarin tsallaka tekun Bahar Rum ya karu a watannin baya-bayan nan.

Kungiyoyin agaji sun zargi masu gadin gabar ruwan Libya da hukumomin Turai da gazawa wajen sauke nauyin da ke kansu na ceto rayukan bakin.

Munyi kokari amma mun nemesu mun rasa

Sai dai wani jami’in tsaron gabar ruwan Libya ya bayyannawa kamfanin dillacin labarai na Associated Press cewa sunyi kokarin neman jirgin amma suka rasa saboda karancin kayan aikinsu.

SOS Mediterranee, wata kungiyar da ke aikin ceto da jirgin Ocean Viking, ta bayyana cewa ta hango kwale-kwalen roba a  yammacin Alhamis wanda ke dauke da kusan mutane 130, a Tekun na Bahar Rum da ke arewa maso gabashin Tripoli babban birnin kasar Libya .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.