Isa ga babban shafi
Mozambique-Rikici

Al'ummar Palma dubu 5 da rikici ya kora sun samu mafaka a cikin Mozambique

Majalisar Dinkin Duniya ta ce 'yan gudun hijira sama da 5,000 da suka gudu domin tsira da rayukan su daga rikicin da ake yi a garin Palma da ke kasar Mozambique yanzu haka sun samu mafaka.

Wasu tarin 'yan gudun hijirar Mozambique da suka samu mafaka.
Wasu tarin 'yan gudun hijirar Mozambique da suka samu mafaka. © MSF/AP
Talla

Mai magana da yawun hukumar kula da kaurar baki ta Majalisar Sandra Black ta ce ya zuwa ranar Talatar da ta gabata, sun kidaya mutane dubu 5 da 360 da suka isa yankunan Nangade da Mueda da Montepuez da kuma Pemba.

Rahotanni sun ce mutane da dama sun mutu sakamakon hare haren da 'yan tawayen yankin suka kai wadanda ke ikrarin jihadi.

Rikicin 'yan bindigar ya yi sanadiyar raba mutane kusan 670,000 daga muhallin su a yankin dake da arzikin iskar gas.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.