Isa ga babban shafi
Muhalli-Sauyin Yanayi

Guguwar Eloise ta rushe gidaje fiye da dubu 5 a Mozambique

Hukumomin agaji a Mozambique sun ce dubban mutane sun rasa muhallansu sakamakon guguwar Eloise da ta ratsa kasar a karshen mako.

Hoton da asusun UNICEF ya dauka a ranar 24 ga Janairun 2021, dake nuna ambaliyar ruwan da guguwar Eloise ta haddasa a yankin Buzi dake kasar Mozambique
Hoton da asusun UNICEF ya dauka a ranar 24 ga Janairun 2021, dake nuna ambaliyar ruwan da guguwar Eloise ta haddasa a yankin Buzi dake kasar Mozambique Bruno Pedro / UNICEF / AFP
Talla

Rahotanni sun ce guguwar dake gudun kilomita 150 kowacce sa’a, dauke kuma da ruwan sama, ta afkawa birnin Beira dake gabar ruwa, abinda yayi sanadin raba mutane akalla dubu 7 da gidajensu, yayin da gidaje sama da dubu 5 suka rushe.

Hukumar again gaggawa tace mutane 6 sun mutu a hadarin, kana wasu 12 sun jikkata.

Shekaru biyu da suka gabata dai guguwar Idai ta tafka mummunar barna a garin na Beira dake gabar ruwa, inda ta salwantar da rayukan mutane da dama da kuma janyo hasarar dimbin dukiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.