Isa ga babban shafi
Sudan-MDD

Rikicin Sudan ta Kudu ya zarce na yakin basasar shekaru 5 - MDD

Wani rahoton majalisar dinkin duniya ya ce rikicin da ke ci gaba da ta’azzara yanzu haka a yankuna da dama na Sudan ta Kudu, shekara daya bayan sanya hannu a yarjejeniyar kawo karshen yakin basasa da aka shafe shekaru 5 ana yi, ya dara na lokacin yakin kansa.

Dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Darfur.
Dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Darfur. Reuters
Talla

Rahoton da hukumar kare hakkin dan adam ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya ce kungiyoyi masu daukar makamai sun zafafa hare hare a kan fararen hula, kuma suna yi ne tare da nuna kabilanci, kuma da goyon bayan gwamnati da dakarun ‘yan adawa.

Shugaban hukumar a Sudan, Yasmin Sooka ta ce rikicin ya zarce wanda aka yi fama da shi daga shekarar 2013 zuwa 2019, tana mai cewa masu hannu a wannan rikici su na yi ne saboda tunanin cewa babu wani mataki da za a dauka a kansu.

An kiyasta cewa yakin basasan da ak gwabza daga shekarar 2013 zuwa 2018 ya lakume rayukan sama da mutane dubu 400, yayin da miliyoyi mutane na kokarin farfadowa daga radadinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.