Isa ga babban shafi
Liberia

Dan asalin Najeriya ya katse aikinsa da shugaban Liberia

Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Liberia wanda kuma dan asalin Najeriya ne, Ndubuisi Nwabudike ya sauka daga mukaminsa sakamakon zargin cewar ya bi ta bayan-gida wajen samun takardar zama dan kasa.

George Weah Shugaban kasar Liberia
George Weah Shugaban kasar Liberia Photo: Ludovic Marin/Pool/AFP
Talla

Bayan takaddamar da ta kaure kan zargin, kotun kolin kasar ta gabatar da hukunci kan cewar Nwabudike bai saba ka‘ida ba wajen karbar takardun zama ‘dan kasa, amma hakan bai hana shi gabatar da takardar murabus dinsa ba.

Jami’in ya rubuta wa shugaban kasa George Weah wasikar cewar ba ya bukatar ci gaba da  zamansa kan kujerar don kauce wa  haifar da matsalar da za ta hana shugaban gudanar da ayyukansa, saboda haka ya sauka daga mukamin.

Nwabudike ya kwashe lokaci yana gudanar da bincike kan ayyukan cin hanci da rashawa a kasar a matsayinsa na lauya, kafin shugaban kasa Weah ya nada shi ya shugabanci hukumar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.