Isa ga babban shafi
Afrika

Afirka ta Tsakiya ta saka dokar ta baci a fadin kasar

Gwamnatin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya ta saka dokar ta baci na kwanaki 15 a dai-dai lokacin da ‘Yan tawayen kasar suka kutsa kai birnin Bangui da nufin kiffar da zababben shugaban kasa Faustın Archange-Touadera.

Jami'an tsaro na gudanar da bincike a wani shigen shiga birnin Bangui na Afrika ta Tsakiya
Jami'an tsaro na gudanar da bincike a wani shigen shiga birnin Bangui na Afrika ta Tsakiya ISSOUF SANOGO / AFP
Talla

Mai magana da yawun fadar shugaban kasa Albert Yaloke Mokpeme ya ce dokar ta shafi yankin kasar baki daya zata kwashe kwanaki 15 tana aiki.

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya a kasar ya bukaci kwamitin sulhu da ya kara yawan dakarun samar da zaman lafiya dake aiki a kasar saboda barazanar ‘yan Tawayen.

Ana zargin tsohon Shugaban kasar Francois Bozize da kotun fasalta kudin tsarin mulkin kasar da yi watsi da takarar sa da tallafawa kungiyoyin yan tawaye a wannan tafiya don kwace ikon Bangui daga hannun Shugaban kasar Touadera.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.