Isa ga babban shafi
Sudan

Adadin wadanda suka mutu a rikicin kabilancin Sudan ya zarta 80

Rahotanni daga Sudan na cewa rikicin kabilanci da ake ci gaba da yi a yankin Dafur da ke yammacin kasar ya lakume rayukan mutane 80 ya zuwa yanzu.

Dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya
Dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya UN Photo/David Manyua
Talla

Rikicin da ya barke a ranar Asabar tsakanin ‘yan kabilar Massalit da Larabawa, makiyaya a garin El Geneina ranar Asabar, na zuwa ne makonni 2 kacal bayan da Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar Tarayyar Afrika suka kawo karshen aikin kiyaye zaman lafiya da suka shafe shekaru 13 su na yi a yankin Dafur.

Rikicin ya kazanta, inda kungiyoyi masu dauke da makamai a yankin suka shiga lamarin, wanda ya kai ga rusa gine gine da gidaje da dama.

A ranar Asabar, Firaministan Sudan Abdalla Hamdok ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa ya tura tawaga mai karfi, ciki har da jami’an tsaro yankin na yammacin Dafur da zummar kawo karshen zub da jinin da ake yi.

A ranar Lahadi jagoran gwamnatin Sudan Abdel Fattah al-Burhan, ya gana da hukumomin tsaron kasar don bin kadin rikicin da ake a yankin na Dafur.

Kungiyar kwararun Sudan, wacce karkashinta aka gudanar da zanga zangar da ta yi sanadin faduwar gwamnatin Omar Al – Bashir a watan Disamban 2018 ta koka da yadda tashin hankalin ya shafi sansanonin ‘yan gudun hijir a yanki.

A ranar 31 ga watan Disamban da ya gabata ne majalisar dinkin duniya ta kawo karshen aikin kiyayen zaman lafiya da ta ke yi a yankin Dafur bayan shekaru 13.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.