Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Zimbabwe ta ayyana dokar hana zirga-zirga saboda Korona

Gwamantin Zimbabwe daga jiya asabar ta aiwatar da dokar hana zirga-zirgar jama’ar bayan da aka fuskanci yawaitar masu kamuwa da cutar Coronavirus.

Birnin Harare na kasar Zimbabwe
Birnin Harare na kasar Zimbabwe Jekesai NJIKIZANA / AFP
Talla

A wannan sabuwar dokar gwamnatin kasar na bukatar mutane su  takaita yawan masu halartar  jana’izza, banda haka ,hukumomin sun haramta taruruka na aure, biki, taruruka a mujami’u, gidajen cin abinci, gidajen rawa na tsawon wata daya.

Mataimakin Shugaban kasar dake da mukamin Ministan kiwon lafiyar kasar Zimbabwe ne ya fitar da wannan sanarwa.

A yanzu haka kasar na da kusan mutane 14.084 da suka kamu da kwayar cutar,yayinda 369 suka mutu a kasar ta Zimbabwe,kasar da tattalin arzikin ta ya kama hanyar rushewa tun farkon shekara ta 2000.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.