Zimbabwe
Ana aikin ceto a Zimbabwe domin zakulo mutanen da kasa ta birne
Hukumomin Zimbabwe sun ce ana gudanar da aikin ceto bayan da wasu tarin ma’aikatan dake hakar ma’adinai suka makale a cikin rami sakamakon zabtarewar kasa a wani tsohon rami.
Wallafawa ranar:
Talla
Jami’an gwamnatin kasar sun ce anyi nasarar zakulo akalla mutane 6 daga cikin sama da 20 dake cikin ramin.
Hakar ma’adinai ba tare da izini ba ya zama ruwan dare a sassan kasar sakamakon rashin aikin yi da kuma annobar korona.
Allah Ya wadata Zimbabwe da zinare da lu’u lu’u.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu