Gwamnatin Habasha ta tura da karin sojoji yankin Benishangul-Gumuz
Bayan kisan mutane 100 a kauyen Bekoji dake yankin Benishangul-Gumuz, a yammacin kasar ta Habasha gwamnatin tarayya ta baza sojoji masu yawa a yankin.
Wallafawa ranar:
Kisan na zuwa a wani lokaci da kungiyoyi kare hakkokin bil Adam ke ci gaba da kira ga kungiyoyi dake fada da juna a kasar na ganin sun kai zuciya nisa don kaucewa fadan kabilanci.
Wannan kisan na zama wani zubar da jinni mafi muni tsakanin kabilun kasar , wadanda aka kashen yan kabilar amhara, oromo da shinasha ne ,kisan da ake zargin yan kabilar gumuz da aikatawa. Masharhanta dai na danganta wannan kisan da ya fi muni wanda firaminista abiy ahmed ya yi Allah wadai da shi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu