Isa ga babban shafi
Afrika

kasashen Sudan da Habasha sun fara tattaunawa don shawo kan rikicin dake tsakanin su

Gwamnatocin kasashen Sudan da Habasha sun fara tattaunawa don shawo kan rikicin da bangarorin biyu suka fuskanta cikin makon jiya game da kan iyakarsu.

Wasu 'Yan gudun hijirar Habasha dake neman mafaka a makwabta
Wasu 'Yan gudun hijirar Habasha dake neman mafaka a makwabta RFI/Eliott Brachet
Talla

Wasu rahotanni sun bayyana yadda dakarun Habasha suka farwa Sojin Sudan da ke tsaron kan iyaka tare da kashe 4 baya ga jikkata wasu 20 a makon jiya.

A watan da ya gabata ,Majalaisar Dinkin Duniya tace Sudan na bukatar akalla dala miliyan 150 domin taimakawa yan gudun hijirar da suka fito daga Habasha sakamakon tashin hankalin dake gudana a Yankin Tigray.

Shugaban hukumar kula da Yan gudun hijira na Majalisar Filippo Grandi ya bayyana haka bayan ya ziyarci inda aka tsugunar da Yan gudun hijira akalla 43,000 da suka samu mafaka a cikin kasar.

Tuni dai mataimakin Firaministan Habasha Demeke Mekonnen ya isa birnin Khartoum don tattaunawa kan rikicin tare da bayar da hakuri.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.