Hukumar zaben Habasha ta shirya don tunkarar zaben kasar
Hukumar zaben Habasha ta sanar da shirye-shiryenta na tunkarar zabe a shekara mai kamawa bayan dage shi a cikin watan Mayun da ya gabata sakamakon tsanantar rikice-rikice da kuma annobar Koronavirus.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta sanya watan Yunin badi a matsayin lokacin da za a gudanar da zaben kasar, duk da cewa bangaren adawa na ci gaba da zargin yadda gwamnati ke kashe musu gwiwa kan zaben.
Rikici Tigray a cewar hukumomin kasar Sudan ya tilastawa yan kasar Habasha 11,000 tsallakawa zuwa kasar su domin kaucewa tashin hankalin dake gudana a Tigray.
Hukumar kula da yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana taimakawa wadannan yan gudun hijira 7,000, yayin da yawan su ke dada karuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu