Afrika-Coronavirus
Adadin mutanen da suka kamu da cutar COVID-19 sun zarce 40,000 a Ghana
Gwamnatin kasar Ghana tace adadin mutanen da cutar COVID-19 ta kama a cikin kasar sun kai 40,097, yayin da 206 daga cikin su sun mutu.
Wallafawa ranar:
Talla
Ma’aikatar lafiyar kasar tace yau juma’a an samu sabbin mutane 455 da suka harbu da cutar, yayin da aka sallami karin mutane 254 da suka warke, abinda ya kawo adadin wadanda suka warke baki daya zuwa 36,638.
Kasar Ghana na daya daga cikin kasashen da suke sahun gaba a Afirka wajen yawan mutanen da suka kamu da cutar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu