Isa ga babban shafi
Najeriya-Lagos

COVID 19: Za a sake bude wuraren ibada a Lagos

Gwamnan Legas a Najeriya, Babajide Sanwo-Olu ya bada umarnin sake bude wuraren ibada a daukacin jihar, bayan da suka shafe watanni a rufe, domin dakile yaduwar annobar coronavirus.

Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, tare da mataimakinsa Obafemi Hamzat daga hadu, sai kuma kwamishinansa na lafiya Farfesa Akin Abayomi.
Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, tare da mataimakinsa Obafemi Hamzat daga hadu, sai kuma kwamishinansa na lafiya Farfesa Akin Abayomi. LASG
Talla

Yayin sanar da matakin a yau asabar, Sanwo-Olu ya ce matakin sake bude wuraren Ibadar zai soma aiki ne daga 7 ga watan Agustan da muka shiga, amma da sharadin kashi 50 cikin 100 na adadin mutanen da filaye ko gine-ginen da wuraren ibadar za su iya dauka ke da izinin shiga cikinsu.

Gwamnan na Legas ya kuma sassauta dokar da ta haramta taron sama da mutane 20 zuwa sama da mutane 50.

Sanwo-Olu ya kuma shawarci dattawa masu shekaru 65 zuwa sama da su kaurce wa wuraren ibada.

A watan Maris ne hukumomin Legas, birni mafi girma a Najeriya mai mazauna miliyan ashirin suka rufe coci coci da masallatai, wuraren shakatawa da sauransu, a kokarin d suke na dakile yaduwar cutar coronavirus.

Ya zuwa yanzu cutar ta harbi mutane dubu 43 da dari da 51, ta kuma kashe dari 8 da 79 tun da ta shiga Najeriya a watan Fabrairu.

Jihar Legas ce cutar ta fi kamari a Najeriya, inda mutane dubu 15 suka harbu, dari da 92 suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.