Isa ga babban shafi
Tanzania

Amurka ta zargi Tanzania da boye adadin masu cutar corona

Shugaban John Magafuli na Tanzania yace a wata mai kamawa, wato 1 ga Yuni, za a bude ilahirin manya da kananan makarantun kasar, zalika za a koma wasanni, bayan fuskantar dokar killace jama’a.

Shugaban kasar Tanzania John Pombe Magufuli.
Shugaban kasar Tanzania John Pombe Magufuli. REUTERS/Thomas Mukoya/File Photo
Talla

Magafuli yace addu’o’i ne suka ceto kasar daga tsanantar annobar ta coronavirus.

Masu caccakar matakin shugaba Magafuli na ganin gwamnatinsa na boye adadin masu dauke da cutar ga duniya ne, inda a nasa bangaren ofishin jakadancin Amurka a kasar yace akwai mutane masu yawa da annobar ke kashewa amma gwamnatin ta Tanzana ta gaza daukar matakin basu kariya.

Makwanni 3 kenan dai rabon da Tanzania da sanar da adadin masu dauke da cutar ta coronavirus, bayan mutuwar mutane 16, daga cikin mutum 480 da gwamnati ta sanar sun kamu da ita.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.