An gaza wadata Najeriya da wutan lantarki duk da kashe makudan kudi da aka yi
Wallafawa ranar:
‘Yan Najeriya na cigaba da bayyana shakku dangane da yunkurin gwamnatocin da suka gabata da kuma mai ci wajen warware matsalar samar da wutar lantarki wanda yayi sanadiyar karyewar wasu kamfanoni da kuma yin illa ga masu kananan masana’antu.Bayan kwashe shekaru 20 ana kashe makudan kudade har yanzu samar da wutar ya gagara, musamman daga bangaren kamfanonin dake raba wutar, matakin da ya sa wani dan Majalisa ya bukaci haramta shigar da janareta kasar ko hakan zai sa gwamnati ta dada jajircewa wajen samar da wutar.Dangane da wannan matsala, mun tattauna da Alh Isa Tafida Mafindi, masanin tattalin arziki, kuma ga tsokacin da yayi kan yunkurin samar da wutar.
An gaza wadata Najeriya da wutan lantarki duk da kashe makudan kudi da aka yi
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu