Isa ga babban shafi
Burkina Faso

'Yan bindiga sun sake kai farmaki a Burkina Faso

Hukumomin tsaron Burkina Faso sun ce fararen hula 4 sun rasa rayukansu a wani sabon hari da aka kai yankin arewacin kasar.

Wasu jami'an sojin kasar Burkina Faso.
Wasu jami'an sojin kasar Burkina Faso. AFP/Getty Images
Talla

An dai kai farmakin jiya asabar ne a garin Samboulga dake lardin Lorum, kwana guda bayan halaka mutane 16 da mayaka masu ikirarin jihadi suka yi yayinda suka ibada a babban masallacin garin Salmossi.

Har yanzu dai babu Karin bayani kan maharan, daga hukumomin tsaron Burkina Fason, zalika babu wata kungiya da ta dauki alhakin hare-haren.

A shekarar 2015, Burkina Faso ta soma fuskantar tsanantar hare-haren mayaka masu da’awar Jihadi, musamman a yankunan arewaci da kuma gabashin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.