Isa ga babban shafi

Najeriya na iya katse lantarkin da ta ke bai wa Nijar Togo da Benin

Kasashen Nijar Togo da Jamhuriyar Benin ka iya fuskantar karancin lantarki kowanne lokaci daga yanzu matukar basu dauki matakin biyan bashin wutar lantarkin da Najeriya ke binsu ba.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari Twitter/Asorock
Talla

Najeriya wadda ke fuskantar matsalar wutar lantarki a yankunanta tsawon lokaci yanzu haka ta kafa wani kwamiti da zai gano abinda ya hana ruwa gudu a wannan fanni.

Sai dai bayan gudanar da binciken kwamitin ya bayyana cewa babbar matsalar da ke hana ruwa gudu wajen samarwa kamfanonin kasar wadataciyar wutar da zasu dogara bai wuce nauyin da ta ke dauka wajen bai wa wasu kasashen ketare lantarkin ba.

A cewar kwamitin kamfanin samar da lantarki na kasar Nijar Nigelec da kuma na Benin Ceb sun gaza biyan tarin basukan da Najeriyar ke binsu wanda da kudaden za ta yi amfani wajen inganta bangaren lantarkin na ta.

Tun kafin yanzu dai, Najeriyar ta yi barazanar katse lantarkin da ta ke bai wa kasashen 3 duk da sanadin tarin bashin da ta ke bin kasashen da suka gaza biya tsawon lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.