Isa ga babban shafi
Sudan

An girke sojoji a babban birnin Sudan

Rundunar Sojin Sudan ta girke jami’anta a birnin Kahrtoum a daidai lokacin da masu zanga-zanga ke bukatar sojojin kasar da su tsoma baki kan tilasta wa shugaba Omar al-Bashir sauka daga mukaminsa.

Masu zanga-zangar na bukatar kawo karshen mulkin shugaba Omar al-Bashir da ya shafe shekaru kusan 30 kan karaga
Masu zanga-zangar na bukatar kawo karshen mulkin shugaba Omar al-Bashir da ya shafe shekaru kusan 30 kan karaga REUTERS/Stringer
Talla

Rahotanni na cewa, wasu daga cikin sojojin sun nun alamar bai wa masu zanga-zangar kariya bayan wasu jami’an tsaro na daban sun harba hayaki mai sa kwalla kan masu zanga-zangar da suka yi zaman dirshen,

Shaidu sun ce, sojojin sun yi fatattaki wasu manyan motoci da ke cilla barkonon-tsohuwa kan masu zanaga-zagar.

Babu cikakken bayani kan jami’an tsaron da suka cilla barkonon-tsohuwar, amma  bayanai na cewa, ma’aikata ne a Hukumar Leken Asirin Kasar.

Masu zanga-zangar na fatan sojojin za su yi wa shugaban kasar juyin mulki bayan ya shafe kusan shekaru 30 a kan karagar mulki.

Kawo yanzu, shugaba al-Bashir ya ki amincewa da bukatar kafa gwamnatin rikon kwarya duk da tsawon lokacin da aka shafe na gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.