Isa ga babban shafi
Sudan

Al'ummar Sudan na fatan samun canjin Shugabanci

Ministan Harkokin cikin gida na kasar Sudan Bushara Juma ya sanar da cewa mamata sakamakon zanga-zangan kasar sun kai 6 ya zuwa yau Littini.Ministan ya ce akwai mutane 15 da wasu jamian tsaro 42 da suka jikkata.

Masu zanga-zanga a kasar Sudan
Masu zanga-zanga a kasar Sudan AFP/A. Shazly
Talla

Ga duk alamu, wasu daga cikin sojojin sun nuna alamar bai wa masu zanga-zangar kariya bayan wasu jami’an tsaro na daban sun harba hayaki mai sa kwalla kan masu zanga-zangar da suka yi zaman dirshen,

Shaidu sun ce, sojojin sun yi fatattaki wasu manyan motoci da ke cilla barkonon-tsohuwa kan masu zanaga-zagar.

Masu zanga-zangar na fatan sojojin za su yi wa shugaban kasar juyin mulki bayan ya shafe kusan shekaru 30 a kan karagar mulki.

Kawo yanzu, shugaba al-Bashir ya ki amincewa da bukatar kafa gwamnatin rikon kwarya duk da tsawon lokacin da aka shafe na gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.