Al'ummar Sudan na fatan samun canjin Shugabanci
Ministan Harkokin cikin gida na kasar Sudan Bushara Juma ya sanar da cewa mamata sakamakon zanga-zangan kasar sun kai 6 ya zuwa yau Littini.Ministan ya ce akwai mutane 15 da wasu jamian tsaro 42 da suka jikkata.
Wallafawa ranar:
Ga duk alamu, wasu daga cikin sojojin sun nuna alamar bai wa masu zanga-zangar kariya bayan wasu jami’an tsaro na daban sun harba hayaki mai sa kwalla kan masu zanga-zangar da suka yi zaman dirshen,
Shaidu sun ce, sojojin sun yi fatattaki wasu manyan motoci da ke cilla barkonon-tsohuwa kan masu zanaga-zagar.
Masu zanga-zangar na fatan sojojin za su yi wa shugaban kasar juyin mulki bayan ya shafe kusan shekaru 30 a kan karagar mulki.
Kawo yanzu, shugaba al-Bashir ya ki amincewa da bukatar kafa gwamnatin rikon kwarya duk da tsawon lokacin da aka shafe na gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatinsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu