Isa ga babban shafi
Najeriya-Kamaru

'Yan gudun hijirar Najeriya dubu 35 sun samu mafaka a Kamaru

Majalisar Dinkin Duniya tace yanzu haka yan gudun hijirar Najeriya dubu 35 da suka nemi mafaka a kasar Kamaru sakamakon harin da mayakan boko haram suka kai garin Rann na cikin koshin lafiya.

Wasu 'yan Najeriya da rikicin Boko Haram ya tilastawa tserewa zuwa Kamaru.
Wasu 'yan Najeriya da rikicin Boko Haram ya tilastawa tserewa zuwa Kamaru. IRIN News/Monde Kingsley Nfor
Talla

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar, tace sai dai wasu daga cikin wadanda suka samu mafaka a Kamaru na jefa kansu cikin hadari saboda yadda suke takawa da kafa domin komawa garin na Rann.

Jami’in Majalisar dake Kamaru, Allegra Baiocchi, yace ya ga mutane da dama dake zama cikin fargaba a cikin 'yan gudun hijirar saboda yadda aka lalata rayuwar su.

Shi kuwa Geert de Casteele, jami’in hukumar kula da 'yan gudun hijira a kasar ya yaba ne da daukin da kungiyoyin agaji suka kaiwa bakin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.