An samu barkewar cutar Kwalara a jihar Gombe ta Najeriya
Hukumomin Lafiya a jihar Gombe da ke Tarayyar Najeriya sun tabbatar da mutuwar akalla Mutane 5 yayinda wasu 16 kuma yanzu haka ke karbar kulawa a Asibiti sakamakon barkewar cutar Kwalara a wasu sassa na jihar.
Wallafawa ranar:
Dr Nuhu Bile wanda ke matsayin mukaddashin shugaban sashen kula da cutuka masu saurin yaduwa na jihar ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya cewa tun a cikin watan Octoba aka fara samun wadanda suka kamu da cutar ta Kwalara.
Dr Bile ya ce cutar ta fi tsananta ne a yankin Kembu na karamar hukumar Balanga da ke jihar yayinda yanzu haka marasa lafiyan ke ci gaba da karbar kulawar gaggawa don ceto rayukansu.
A cewarsa a aikin hadin gwiwar da suka gudanar da hukumar lafiya ta duniya WHO a yankin da aka samu bullar cutar sun yi nasarar magance cutar kan mutane akalla 70 yayinda wasu daga ciki suka mutu tun a watan Oktoba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu