Isa ga babban shafi
Mali

Gwamnatin Mali ta tsaida ranar zaben shugaban kasa

Gwamnatin Mali ta bada tabbacin cewa zaben shugabancin kasar zai gudana a ranar 29 ga watan Yuli mai zuwa, idan kuma akwai bukatar gudanar da zaben zagaye na biyu, zai gudana ne ranar 12 ga watan Agusta.

Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita a lokacin da ya ke kada kuri'a a birnin Bamako, yayin zaben kananan hukumomi, a ranar 20 ga watan Nuwamba, 2016.
Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita a lokacin da ya ke kada kuri'a a birnin Bamako, yayin zaben kananan hukumomi, a ranar 20 ga watan Nuwamba, 2016. HABIBOU KOUYATE / AFP
Talla

Sanawar ta zo ne bayan da majalisar kasar ta Mali, ta amince da shirin gwamnati da Fira Minista Soumelou Boubeye Maiga ya gabatar mata.

A jawadalin da gwamnati ta fitar, za’a soma yakin neman zabe daga ranar 7 zuwa 27 na watan Yulin.

Sau da dama gwamnatin Mali ta dage zaben shugabancin kasar tun daga shekarar 2013, saboda fuskantar matsalolin tsaro, a dalilin hare-haren kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi a kasar, wadanda a cikin shekaru biyu da suka wuce, suka bazu daga arewaci zuwa tsakiya, da kuma kudancin kasar.

Kafin wannan lokacin dai, cikin shekarar 2012, kungiyoyin mayakan da ke da alaka da Al Qaeda suka kwace iko da yankin arewacin kasar Mali, kafin daga bisani rundunar soji, a karkashin jagorancin Faransa su kore su daga mafi akasarin yankunan da suka kwace.

A cikin watan Maris da ya gabata ne gwamnatin kasar ta Mali, ta dage zaben larduna da aka shirya gudanar da shi a Afrilu zuwa karshen wannan shekara ta 2018.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.