Isa ga babban shafi
Najeriya-Boko Haram

Ana wata arangama tsakanin Sojin Najeriya da Boko Haram a Maiduguri

Rahotanni daga Maidugurin Najeriya sun ce yanzu haka mayakan boko haram na fafatawa da sojojin kasar a kokarin su na kutsa kai zuwa cikin birinin da nufin kaddamar da hare-haren ta'addanci.

Yanzu haka ana ci gaba da fafatawa tsakanin dakarun sojin Najeriya a kokarin da su ke na dakile mayakan na boko haram daga shiga barikin Giwa don kwato wasu kwamandojin su da ake rike da su.
Yanzu haka ana ci gaba da fafatawa tsakanin dakarun sojin Najeriya a kokarin da su ke na dakile mayakan na boko haram daga shiga barikin Giwa don kwato wasu kwamandojin su da ake rike da su. STEFAN HEUNIS / AFP
Talla

Bayanan da ke fitowa daga garin sun ce, ana ta jin karar musayar wuta tsakanin bangarorin biyu tun karfe 6 na yamma, kuma rahotanni sun ce mayakan na kokarin kutsawa ne cikin barikin sojin Giwa inda ake tsare da kwamandodin su da dama.

Ya zuwa yanzu babu wata sanarwa daga rundunar sojin kasar kan halin da ake ciki, amma kuma mazauna garin da dama sun shaida mana cewar suna cikin halin fargaba sakamakon arangamar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.