Bakonmu a Yau
Sabo Sa'idu masanin siyasar kasashen larabawa akan zaben kasar Masar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:26
Al'ummar kasar Masar suna ci gaba da bayyana gamsuwarsu bayan da aka bayyana shugaba mai ci AbdelFata al-Sisi a matsayin wanda ya sake lashe zaben shugabancin kasar. Zaben dai tamkar wani zakaran gwajin dafi ne ga shugaba al-Sisi wanda ya sha alwashin yakar ta'addanci a fadin kasar. Kan haka ne Abdullahi Isa ya tattauna da Sabo Sa'idu, wani masanin siyasar kasashen larabawa.