Afrika ta Kudu
Jacob Zuma zai gurfana gaban kotu kan Rashawa
Mai Gabatar da kara a kasar Afirka ta kudu ya ce za’a gurfanar da tsohon shugaban kasar Jacob Zuma a gaban kotu, domin tuhumar sa da laifufukan da suka shafi cin hanci da rashawa lokacin da yake rike da shugabancin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Shaun Abrahams, Daraktan gabatar da kararraki na kasar, ya ce bayan nazari kan zargin da ake yiwa tsohon shugaban kasar, ya yanke hukuncin cewar za’a samu nasarar tuhumar tsohon shugaban.
Cikin tuhume tuhumen da za’a yiwa tsohon shugaban sun hada da cin hanci da rashawa da halarta kudaden haramun da kuma almundahana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu