Isa ga babban shafi
Togo Ghana

'Yan Togo na tserewa zuwa Ghana neman mafaka

Hukumar Kula da ‘yan gudun hijira a Ghana ta ce yanzu haka daruruwan ‘yan kasar Togo ne suka tserewa zanga-zangar da ‘yan adawa ke yi domin samun mafaka a kasar.

Al'ummar Togo da ke zanga-zangar adawa da shugabancin Faure Gnassingbé
Al'ummar Togo da ke zanga-zangar adawa da shugabancin Faure Gnassingbé REUTERS/Stringer
Talla

Paddy Tetteh ya ce tun ranar larabar makon jiya ‘yan gudun hijirar suka fara isa Ghanar, kuma yanzu haka adadin su ya kai 300.

Sarkin Chereponi Abdul Razak Tahiru ya ce tuni aka taimakawa bakin da abinci da tabarmi da gidajen sauro.

Tun a Makonni baya ake samun bore daga al'ummar Togo da ke nuna adawarsu da shugabancin Faure Gnassingbe wanda ke mulkin kasar tun 2005.

Mista Gnassingbe ya karbi mulkin kasar ne daga wajen mahaifinsa wanda ya shafe shekaru 38 yana jan ragamar kasar tun 1967.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.