Isa ga babban shafi
Nijar

Nijar ta daure ‘Yan Sanda uku da suka ba dalibi kashi

Wata Kotu a Nijar ta yankewa wasu ‘Yan Sanda uku hukuncin daurin shekara guda a gidan yari saboda samunsu da laifin dukan wani dalibin jami’a lokacin da dalibai ke gudanar da zanga zanga a Niamey.

A shekarar 1990 ne Jami'an tsaron Nijar suka kashe wasu dalibai uku
A shekarar 1990 ne Jami'an tsaron Nijar suka kashe wasu dalibai uku Boureima Hama-AFP
Talla

Kotun ta kuma umurci ‘Yan Sandan su biya tarra sefa miliyan 15 kwatankwacin yuro 23,000 ga dalibin da suka jikkata.

Wani faifan bidiyo da aka dauka ranar gudanar da zanga zangar ya nuna ‘Yan Sandan guda uku na dukan dalibin da suka kama a bayan mota.

‘Yan sanda sun yi arangama da daliban da gudanar da zanga-zangar a watan Afrilu a Niamey.

A watan Fabrairun 2016 daliban Jami’a sun kaddamar da wata babbar zanga-zanga domin tuna kisan wasu dalibai guda uku da Jami’an tsaron Nijar suka yi shekaru 26 da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.