Isa ga babban shafi
Masar

Harin kunar bakin wake ya hallaka sojin Masar sama da 20

Wani harin kunar bakin wake da aka kai kan shingen bincike soji, a arewacin Sinai da ke Masar, ya hallaka akalla jami’an sojin kasar 26.

Wurin binciken ababen hawa da dan kunar bakin wake ya kai hari a yankin Sinai da ke Masar.
Wurin binciken ababen hawa da dan kunar bakin wake ya kai hari a yankin Sinai da ke Masar. TWITTER
Talla

Dan kunar bakin waken yayi amfani da mota, makare da bama-bamai, inda ya danna kai zuwa shingen binciken jami’an sojin a kudancin kauyen Rafah, ya gabza ta, nan take kuma ‘yan bindiga masu yawan gaske suka bude wuta, inda suka raunata sojoji 26 bayan wasu 26 da suka hallaka.

Yayinda take tabbatar da aukuwar harin, rundunar sojin kasar, ta kuma ce jami’anta, sun yi nasarar hallaka mayaka Arba’in daga cikin maharan da suka far musu, wadanda ake zargin ‘yan kungiyar ISIS ne.

Tuni dai kungiyar ISIS da dauki alhakin kai harin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.