Isa ga babban shafi
Janhuriyar Tsakiyar Africa

Gwamnati da 'Yan Tawaye a Janhuriyar Tsakiyar Afrika Sun Amince da Sulhu

Yau ne Gwamnatin kasar Janhuriyar Tsakiyar Afrika da bangaren ‘yan tawayen kasar suka sanya hannu cikin yarjejeniyar tsagaita wuta a wani taron da aka yi a Rome da niyyar kawo karshen tarzoma a fadin kasar. 

Sojan wanzar da zaman lafiya na kasashen Africa dake aiki a Bangui
Sojan wanzar da zaman lafiya na kasashen Africa dake aiki a Bangui EUTERS/Luc Gnago
Talla

Ana sa ran bayan sulhun kungiyoyin dake dauke da makamai za su shiga Gwamnati domin ganin sun daina tada zaune tsaye.

Kasar Janhuriyar Tsakiyar Afrika wadda ake ganin a duniya ita ce mafi koma baya ta fannin komi, na fama da tashe-tashen hankula  musamman na addini tun shekara ta 2013.

Rayukan mutane sama da 100 suka mutu yayinda wasu dubu dari suka tsere daga gidajen su.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.