Mutane 669 suka mutu a rikicin Habasha
Sakamakon wani bincike da aka gudanar ya ce adadin mutane 669 aka kashe a rikicin da aka shafe watanni ana yi a wasu yankuna uku na kasar Habasha, kafin gwamnati ta kafa dokar ta baci.
Wallafawa ranar:
Rahoton binciken wanda aka gabatarwa Majalisa a ranar Talata ya zargi Jami’an tsaro da sakaci a wasu yankunan da aka yi fama da rikicin.
Hukumar kare hakkin bil’adama ta Habasha ce ta gudanar da binciken kuma a cikin rahoton da ta gabatarwa Majalisar kasar ta ce adadin mutane 669 aka kashe a rikicin da aka shafe kusan shekara guda ana yi a wasu yankuna uku na kasar da suka hada da Oromiya da Amhara.
An samu rikici ne bayan zanga-zangar da mutanen yankin suka kaddamar da suka kira ta neman hakkinsu.
Rahoton binciken ya ce adadin masu zanga-zanga 462 da jami’an tsaro 33 aka kashe a rikicin da ya bazu garuruwa 91 a yankin Oromiya inda mutanen yankin ke zanga-zangar kwato yankunansu da suka fada ikon Addis Ababa babban birnin kasar.
A yankin Amhara kuma masu zanga-zangar 110 aka kashe da kuma jami’an tsaro 30.
Shugaban hukumar kare hakkin bil’adama a kasar ta Habasha ya shaidawa majalisa cewa bincikensu ya tabbatar da akwai sakaci daga bangaren jami’an tsaro musamman yadda aka samu turmutsitsi bayan sun harba hayaki mai sa kwalla a gangamin addini.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu