Kungiyoyin yan jaridu a Kamaru na fatar ganin an salami Ahmed Abba
Kungiyoyin yan jaridu a kasar kamaru sun gudanar da wani gangami tare da shigar da koke zuwa ga hukumomin kasar, domin sakin wakili sashen hausa na gidan rediyon Faransa RFI Hausa, Ahmed Abba, da ake tsare da shi yau kusan watanni 17.
Wallafawa ranar:
Kiran kungiyar yan jaridu na zuwa ga duk masu fafutukar kare hakin bil adam a kamaru dama fadin Duniya ga baki daya na ganin sun bayar da hadin kai ga wannan gwagwarmaya domin ganin an salami ahmed Abba.
A anar 4 ga watan janairu shekarar 2017 ne za a sake koma wa kotu kamar dai yada daya daga cikin mamba a kungiyar ta yan jaridu kasar a Kamaru Sule Ono-hiolo ke cewa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu